Tinubu ya dauki alkawarin cewa gwamnatinsa za ta karawa Sarakunan gargajiya karfi a dokar kasa.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dauki alkawarin cewa gwamnatinsa za ta karawa Sarakunan gargajiya karfi a dokar kasa.

Shugaba Tinubu ya ce zai yi aiki da ‘yan majalisar tarayya domin a ba Sarakuna aiki a tsarin mulki.

Shugaban kasar ya dauki wannan alwashi ne wajen taya Mai martaba Oba Victor Kiladejo murnar cika shekara 70 a duniya.

Tinubu wanda ya samu wakilcin Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo zuwa wannan biki da aka shirya, ya jaddadawa Sarakunan gargajiya cewa gwamnati mai-ci za ta yi aiki da su. .

Rahoton ya ce gwamnatin Tinubu ta na ganin Sarakunan gargajiya suna da rawar takawa wajen kawo tsaro da zaman lafiya a kasarsu.

Haka zalika nauyin kare al’adar gargajiya ta rataya ne a kan wadannan Sarakuna.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *