Janar Christopher Musa ya jaddada aniyar rundunar sojin Najeriya na kawo karshen kalubalen tsaro a

Babban hafsan hafsoshin tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya jaddada aniyar rundunar sojin Najeriya na kawo karshen kalubalen tsaro a kasarnan.

Musa ya bayyana haka ne a wata ziyarar bangirma da ya kai wa Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli a yammacin ranar Juma’a a garin Zariya na jihar Kaduna.

Ya kuma ba da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba kalubalen tsaro da kasarnan  ke fuskanta zai zama tarihi, kuma ya nemi a yi wa sojoji addu’ar samun nasara.

Musa tare da wasu manyan hafsoshin soji sun yi ta’aziyyar rasuwar wasu masallata takwas, wadanda suka mutu a wani masallaci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *