Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, a yau za ta fara yajin aikin gargadi na kwanaki biyu bayan ta kaurace wa taron da ta yi da gwamnatin tarayya kan wahalhalun da mambobin kungiyar ke fama dasu a fadin kasar nan sakamakon cire tallafin man fetur.
Wannan dai ya zo ne a daidai lokacin da ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Simon Lalong, a jiya ya yi gargadin cewa yajin aikin zai kara dagula al’amuran talakawan Najeriya, ya kuma bukaci kungiyar NLC da ta yi watsi da matakin.
A ranar Juma’ar da ta gabata ne kungiyar NLC ta sanar da fara yajin aikin gargadi na kwanaki biyu don nuna rashin amincewa da irin wahalhalun da talauci da ake fama da shi a fadin kasar nan.
Lamarin da ke barazana ga rufe tattalin arzikin kasa baki daya a cikin kwanaki 14 na aiki ko kwanaki 21 bayan yajin aikin, idan har aka fara yajin aikin. gwamnati ba ta dauki matakin magance wahalhalun da aka fuskanta a fadin kasar ba.
Da yake jawabi a ranar Juma’a bayan taron NEC, shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce NEC a zamanta na NLC ta yanke shawarar fara aikin rufe kasa baki daya cikin kwanaki 14 na aiki ko kuma kwanaki 21 daga yau har sai an dauki matakin da NLC ta nemi a dauka.
Gwamnati ta yi kokarin shawo kan matsalolin da ake fama da su da talauci da ake fama da su a fadin kasar nan domin ba zamu zuba ido muna ganin yan siyasa su dinga ci da gumimmu ba.