Buhari ya halarci babban taron gidauniyar ci gaban jihar Katsina na 2023

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya halarci babban taron gidauniyar ci gaban jihar Katsina na 2023 da aka gudanar a gidan gwamnati Katsina a safiyar Laraba.

Wannan shi ne karom farko da Buhari ya bayyana a bainar jama’a bayan mika ragamar mulki ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Litinin, 29 ga watan Mayu, 2023.

Gwamnan jihar, Dikko Umaru Radda ne, ya tarbi tsohon shugaban a wajen taron tare da manyan jami’an gwamnati.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *