CBN ya dage takunkumin ajiye kudiadadin Dala dubu goma asusun ajiya na kudaden waje

Babban Bankin Nijeriya ya dage takunkumin ajiye kudi adadin Dala dubu goma asusun ajiya na kudaden waje a wani bangare na gyaran fuska kan harkokin Bankin.

Bankin ya ce, masu asusun suna da ‘yancin ziyartar asusunsu a kowanne lokaci ba tare da kayyadewa ba.

Babban Bankin ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar bayan wani taro da kwamitin
ma’aikatan bankuna a ranar Lahadi.

An yi taron ne don ba da kwarin guiwa ga masu asusun Dala, kan sauye-sauye da Babban Bankin ya yi a kasuwar ‘yan canji na baya-bayan nan da kuma tattaunawa da aiwatarwa da kuma tasirin sauye-sauyen manufofin ga abokan huldar bankuna.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *