Tinubu ya karbi bakuncin Dangote a fadar shugaban kasa

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya karbi bakuncin mai kudin Afrika, Alhaji Aliko Dangote a fadar shugaban kasa da ke Abuja a ranar Juma’a, 16 ga watan Yuni.

Dangote ya shiga jerin manyan masu ruwa da tsakin da suka zaiyarci Shugaban kasa Tinubu tun bayan da ya hau karagar mulki a ranar Litinin, 29 ga watan Mayu.

Sai dai kuma, ba a tabbatar da abun da ganawar tasu ta kunsa ba amma akwai alamu da ke nuna kawai ziyarar ban girma ce ko kuma dai jiga-jigan kasar biyu sun tattauna ne game da yiwuwar hada kai don bunkasa tattalin arzikin Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *