Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa ya ce ‘yan Najeriya za su iya samun cimma nasarori a tare.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa Humwashi Wonosikou ya fitar a ranar Litinin.
Fintiri ya bayyana jin dadinsa kan dimokuradiyyar Najeriya da ba ta karye ba tun bayan komawar mulkin farar hula a shekarar 1999, yana mai bayyana ta a matsayin nasarar samun ‘yanci.
Don haka ya yi afuwa ga fursunoni guda biyu da aka lissafta sunayensu, Adeolu Adumjobi da Ibrahim Babale wadanda ke zaman gidan yari a jihar.