Tinubu ya yi kira ga Gwamnoni dasu hada kai da FG wajen yaki da talauci

Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya yi kira ga Gwamnoni da su hada kai da Gwamnatin Tarayya wajen yaki da talauci a Najeriya.

Shugaban, wanda ya yi wannan kiran lokacin da ya karbi Gwamnonin Najeriya a fadarsa da ke Abuja ranar Laraba ya ce yawan talaucin ba abin da za a lamunta ba ne.

Tinubu ya kuma yi kira ga ’yan siyasa da su manta da bambance-bambancensu su hada gwiwa wajen kakkabe talauci a Najeriya.

Shugaba Tinubu ya kuma ce shugabanci na gari ne zai tabbatar da ci gaban Dimokuradiyya a Najeriya.

Kazalika, ya kuma ba Gwamnonin tabbacin cewa kofarsa za ta zama a bude ga dukkan Gwamnonin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *