Gwamnan Sakkwato ya raba gero ga iyalan wadanda harin’yan bindiga na ranar Lahadi ya shafa.

Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu ya raba gero ga iyalan wadanda harin ’yan bindiga na ranar Lahadi ya shafa.

Gwamnan ya kuma ba da tallafin kudi ga wadanda suka samu rauni ko rasa wata kadara a lokacin harin.

A satin da ya gabata ne ’yan bindiga suka kai hari a wasu kauyukka biyar a Karamar Hukumar Tangaza inda suka kashe mutum 37, wasu da dama suka samu rauni.

Gwamna Ahmad Aliyu ya ziyarci mutanen ne tare da rakiyar mataimakinsa, Idris Muhammad Gobir da Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar da jagoran jam’iyar APC a Sakkwato, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko wanda ya baiyana harin da cewa rashin hankali ne da dakikanci.

Ya bai wa mutanen jihar tabbacin gwamnati ba za ta huta ba har sai ta kare rayuwar mutane da dukiyoyinsu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *