APC ta rushe kwamitin da ta kafa na yaƙin neman zaɓen shugaban a zaɓen 2023.

APC mai mulkin kasa ta rushe kwamitin da ta kafa a bara na yaƙin neman zaɓen shugaban a zaɓen 2023.

Cikin wata sanarwa ta haɗin gwiwa da ta fitar a ranar Asabar, tsakanin Babban Daraktan APC gwamna Simon Bako Lalong da kuma Sakataren kwamitin James Abiodun Falake.

Jam’iyyar ta yi godiya a madadin shugaban yaƙin neman zaɓen 2023 Muhammadu Buhari, ga duka mutanen da suka taimaka aka kai ga nasarar da aka samu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *