Wamakko ya lashe zaɓen sanatan Sokoto ta Arewa

Tsohon gwamnan Sokoto, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya lashe zaɓen sanatan Sokoto ta Arewa, a zaɓen cike giɓi da aka gudanar jiya a wasu sassa na Najeriya.

Magatakarda ya samu nasara ne a kan mataimakin gwamnan Sokoto Mannir Muhammad Ɗan’iya.

Wamakko ya samu ƙuri’a 141,468 yayin da babban abokin takararsa Ɗan’iya ya samu 118,445 a zaɓen, wato bambancin ƙuri’a 23,023 tsakaninsu.

A baya dai, an bayyana zaɓen a matsayin wanda bai cika ba saboda zarge-zargen maguɗi da tashe-tashen hankula da amfani da ‘yan banga wajen tarwatsa zaɓe.

Wamakko ya yi gwamnan jihar Sokoto sau biyu, kuma a 2015 ya ci kujerar sanata ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Yanzu dai ana jiran sakamakon kujerar sanata daga shiyya biyu ta ɗan majalisar dattijai daga jihar Sokoto da suka rage.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *