INEC za ta raba takardun shaidar nasara ga duka wadanda suka lashe zaben Gwamnoni.

Hukumar zabe ta kasa INEC ta ce za ta raba takardun shaidar nasara ga duka wadanda suka lashe zaben Gwamnoni a kasar nan.

A wata sanarwa da ta fitar a daren jiya, INEC ta ce za a mika\ satifiket ga zababbun gwamnoni da wadanda suka lashe zaben majalisar dokoki.

Kwamishinan yada labaran hukumar festus okoye ne ya bayyana hakan inda yace za a fara wannan aiki ne daga ranar 29 zuwa 31 ga watan Maris na shekarar 2023 da muke ciki, a ofisoshin hukumar INEC da ake dasu a jihohi.

Sashe na 72 (1) ya wajabtawa hukumar kasar bada takardar shaida ga ‘yan takaran da suka yi nasara, za ayi hakan ne kafin a zarce kwanaki 14.

A dalilin haka, Okoye ya ce daga ranar Laraba zuwa Juma’a mai zuwa, zababbun Gwamnoni da ‘yan majalisun jiha za su karbi takardar nasararsu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *