Kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da ayyuka na musamman ya yi alwashin yin doka da zata taimaka wajen kafa wata hukuma da zata kyautata wa talakawa da masu karamin karfi, to sai dai masana na ganin akwai abin dubawa domin sauran hukumomin da ake da su ba a tafiyar da ayyukansu yadda yakamata.
Yusuf ya ce an gabatar da kudurin ne domin ana so a bar wani muhimmin abu bayan wa’adin gwamnati mai ci, saboda an ga alfanun shirin wanda aka kwashi shekaru kusan bakwai ana yi kuma mutane suna samun tallafi.
Shugaban shirin tallafa wa talakawa na kasa Dr. Umar Buba Bindir, ya ce mutane da yawa sun amfana da shirin.
An kasa shirin zuwa bangarori hudu, da farko akwai matasa miliyan daya da dubu dari biyar wadanda basu da aiki, ana koya masu sana’a sannan a basu tallafi.
Akwai kuma yaran talaka da ake ciyar wa a makarantu su miliyan goma zuwa miliyan sha biyu, da mata miliyan uku masu kananan sana’o’i da ake basu bashin kudi dubu hamsin zuwa dubu dari uku, sannan akwai gidaje miliyan biyu da ke dauke da mutane miliyan goma da ake ba su naira dubu 5 domin su samu abinci.
Bindir ya ce shiri ne da ya kamata ya dore amma a karkashin hukuma mai zaman kanta.
To amma ga Kwararre a fannin tattalin arziki Yusha’u Aliyu, ya na ganin kafa hukuma a yanzu ba daidai ba ne.