Emiefele nemi afuwar ƴan Najeriya kan matsalar da ake fuskanta wajen tura kuɗi ta intanet

Gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emiefele, ya roki afuwar ƴan Najeriya kan matsalar da ake fuskanta wajen tura kuɗi ta intanet.

Emefiele ya bayyana haka ne a taron kwamitin tsare-tsare kan harkokin kuɗi da aka gudanar a Abuja, inda ya tabbatar wa ƴan ƙasar cewa za a magance matsalar nan ba da jimawa ba.

A cewarsa, sashin da ke kula da biyan kuɗaɗe na babban bankin, ya yi iya kokarinsa don tabbatar da cewa an magance matsalar, a daidai lokacin da ƴan Najeriya ke ci gaba da fuskantar wahalhalu wajen aika kuɗi da wayoyinsu da kuma a na’urar cirar kuɗi ta POS.

An soma fuskantar matsalar ne tun bayan da gwamnati ta kaddamar da batun sake fasalta kuɗi wanda kuma ya janyo ƙarancin takardun kuɗi a faɗin ƙasar.

A taron, gwamnan babban bankin ya kuma yi magana kan rashni wadatuwar takardun kuɗi a ƙasar saboda sake fasalin naira, inda ya ce bankin zai ci gaba da buga sabbin takardun kuɗi domin su wadatu musamman ma a kasuwanni.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *