Shugaban Congo ya sanar da hutun kwanaki uku a matsayin na zaman makoki kan kisan kiyashin da aka yi a gabashin ƙasar.

An daɗe ba a samu irin wannan rikicin ba a yankin da lamarin ya faru amma Shugaba Feliz Tshisekedi ya bayyana cewa sama da mutum ɗari ne aka kashe a ƙauyen Kishi-she.

Gwamnatin ƙasar ta ɗora alhakin kisan kan ƴan tawayen M23, duk da cewa sun musanta zargin.

An ta samun ƙarin rikice-rikice tun bayan da Jamhuriyyar Congo da Rwanda suka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a makon da ya gabata.

Congo da Amurka da Majalisar Ɗinkin Duniya duk sun zargi Rwanda da goyon bayan yan tawayen M23 duk da cewa Rwandan ta musanta hakan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *