Hukumar INEC ta sanar da ranakun da za ta rabar da katinan zaɓe a faɗin ƙasar.

A wata sanarwa da hukumar ta wallafa shafinta na Tuwita ta ce ta saka ranar Litinin 12 ga watan Disamba zuwa Lahadi 22 ga watan Janairun 2023 a matsayin ranakun da za ta rabar da katinan zaɓen a ofisoshinta da ke faɗin ƙananan hukumomin ƙasar 774.


Tuni dai hukumar ta sanar da ranar 25 ga watan Fabrairun 2023 a matsayin ranar da za ta gudanar da zaɓen shugaban ƙasar tare da na ‘yan majalisun dokoki.

Yayin da za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi ranar 11 ga watan Maris ɗin 2023.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *