Mayakan ta’addancin Boko Haram sama da 70 sun rasa rayukansu sakamakon neman tserewa daga luguden sojin Najeriya.

Sama da mutum 70 da ake zargin ‘yan Boko Haram ne ruwa yayi awon gaba da su a a wani rafi bayan luguden wutan da dakarun Operation Hadin Kai suka yi a jihar Borno, majiyoyi suka tabbatar.

An tattaro cewa, sojojin Najeriya tare da hadin guiwar kungiyar tsaron farar hula, JTF, sun halaka sama da ‘yan ta’addan Boko Haram 20 a kauyen Sheruri dake karamar hukumar Bama ta jihar Borno a ranar Alhamis.

Majiyoyi sun ce bayan farmakin Sheruri, wadanda suka tseren ruwa yayi awon gaba da su a rafin dake kusa da kauyen Dipchari dake karamar hukumar Bama a ranar Juma’a, Daily Trust ta ruwaito.

‘Yan ta’addan sun tafka mummunar asara, sun rasa rayukan sama da mayaka 70 a kusa da kauyen Dipchari. A halin yanzu da muke magana, mutane da yawa daga cikin mayakan babu su babu dalilinsu,” majiyar tsaro ta tabbatar”.

“Da safiyar yau wurin karfe 8:30 na safe suka yi jana’izar sama da mayaka 50 a kauyen Dipchari kuma suna cigaba da neman gawawwakin sauran ‘yan ta’addan”.

“Sun samo gawawwaki masu yawa daga rafin amma har yanzu akwai mayakan da ba a gani ba,” majiyar tace”.

Har yanzu babu takardar da ta fito a hukumance daga rundunar sojin Najeriya kafin rubuta wannan rahoton, amma jama’a da yawa daga yankin sun tabbatar da wannan cigaban.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *