Mai Shari’a Tanko Muhammad Ya Ajiye Mukaminsa Na Babban Jojin Najeriya. 

Babban jojin Najeriya, Mai shari’a Tanko Muhammad, ya yi murabus, kamar yadda gidan talabijin na Channels ta ruwaito a ranar Litinin.

Majiyoyi sun shaida wa gidan talabijin na Channels cewa Mai Shari’a Muhammad ya yi murabus ne a daren Lahadin da ta gabata, saboda rashin lafiya a matsayin dalilin yanke hukuncin.

Har ila yau, bayanai sun nuna cewa ana ci gaba da shirye-shiryen rantsar da babban alkalin kotun kolin kasar mai shari’a Olukayode Ariwoola a matsayin babban jojin Najeriya na riko.

Rahotanni sun ce nan ba da jimawa ba za a fitar da sanarwar a hukumance.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *