Rundunar yan sandan Najeriya ta karrama wani jami’inta da ya tsinci makuden kudi a sansanin alhazai ya mayarwa mai shi.

Ya bayyana cewa Mande na aiki ne a Hukumar Jin Dadin Alhazai lokacin da ya tsinci dalla 800 mallakar wata maniyaciyya, Hajiya Hadiza Usman.

“Yayin da ya ke aikinsa a sansanin mahajjata, PC Mande ya tsinci $800 a kasa ya kuma mayarwa Direkatan Hukumar Alhazai, Alhaji Sada Salisu Rumah. “PC Mande ya bayyana cewa tsoron Allah ne yasa ya mayarwa hukumar alhazai kudin domin a mayarwa mai shi.

“Salisu Rumah ya yaba wa dan sandan saboda halin gaskiya da amana,” ya kara da cewa. A cewar Isah, kwamishinan yan sanda ya ji dadin gaskiyar da Mande ya nuna ya kuma yi kira da sauran yan sanda su yi koyi da shi.

anin-alhazai/

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *