Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wani taro su tare da Kansilolinsu kan sha’anin tsaron Jihar.
Offishin mai bai wa Gwamna Shawara kan harkokin tsaro karkashin Alhaji Ibrahim Muhammad Katsina ne ya shirya taron domin duba matsalar tsaron da ta addabi Jihar.
A cewar Masari, wajibi ne su fito su kare tare da ceto yankunan nasu ba tare zaman jiran sai an nemo su ko an kawo masu dauki daga wani waje ba.