Mai magana da yawun hukumar, Mrs Hauwa Mohammed cikin wata sanar da ta fitar, a ranar Lahadi a Kaduna ta ce hukumar ta yi wa fiye da malamai 300000 gwajin cancantar a watan Disambar 2021.
Ta ce an kori malamai 2,192 na frimari ciki har da shugaban kungiyar malamai na kasa, NUT, Mr Audu Amba, saboda kin rubuta jarrabawar ta cancanta.
Ta ce an sallami malamai 165 cikin 27662 da suka rubuta jarrabawar saboda ba su ci ba.
Idan za a iya tunawa gwamnatin a 2018 ta sallami malamai 21,780 wadanda suka fadi jarrabawar, ta maye gurbinsu da wasu sabbin malamai 25,000 da aka yi wa gwajin sosai.
A watan Disambar 2021, hukumar ta kuma sallami malamai 233 kan malakar takardun kammala karatu na bogi.