`Yan takara goma sha shida ne suke fafatawa a zaben.
Duk wanda ya yi nasara a zaɓen zai maye gurbin gwamna mai barin gado Kayode Fayemi na Jam’iyyar APC, wanda a cikin shekarar nan wa’adin mulkinsa zai ƙare.
Tun a watan Janairu ne jam’iyyu suka gudanar da zaɓukan fitar da gwanayensu, kuma sunayen waɗanda hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasar INEC ta tantance ne kawai za su kasance a kan ƙuri’ar zaɓen.
A daidai lokacin da ake gudanar da zaɓe a Jihar Ekiti, wasu daga cikin ƴan kasuwa na ci gaba da gudanar da kasuwancinsu kamar yadda suka saba.
Mata ƴan kasuwa sun taru a kasuwar Esa Oke da ke Ado-Ekiti domin gudanar da kasuwancinsu.
A daidai lokacin da ake gudanar da zaɓe a Jihar Ekiti, wasu daga cikin ƴan kasuwa na ci gaba da gudanar da kasuwancinsu kamar yadda suka saba.
Mata ƴan kasuwa sun taru a kasuwar Esa Oke da ke Ado-Ekiti domin gudanar da kasuwancinsu.