Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno ta cafke wasu bata-gari 87 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban ciki har da masu kai wa Boko Haram bayanai.

Sauran mutanen da rundunar ta cafke sun hada da wadanda ake zargi ’yan fashi ne da barayi da masu aikata fyade da ’yan sara-suka da dai sauransu.


Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar,  Abdu Umar, ya tabbatar da hakan yayin gabatar da wadanda ake zargin a ranar Talata a hedikwatar ’yan sandan da ke birnin Maiduguri.
Ya ce an gurfanar da mutum 67 daga cikinsu a gaban kotu tare da tisa keyarsu zuwa gidan gyaran hali.


Kwamishinan ’Yan Sandan ya bayyana yadda aka cafke wasu da suka yi wa wata yarinya mai shekara 13 fyade.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *