Dan takarar shugaban kasa a jami’yyar APC, Bola Tinubu, ya kaiwa Mataimakin Shugaban kasa Yemi Osinbajo, ziyara a fadar shugaban kasar dake Abuja a daren jiya Alhamis.

Bayan tattaunawa da Osinbajo, ya kuma ziyarci shugaba Muhammadu Buhari.

Tinubu ya samu kuri’u 1,271 a zaben fitar da gwanin jami’yya APC da aka gudanar , inda ya doke sauran ‘yan takara ciki harda Osinbajo wanda ya samu kuri’u 235.


Bola Ahmed Tinubu x V.P Yemi Osinbajo

Ziyarar Tinubu na zuwa ne bayan Osinbajo ya mika sakon taya murna Tinubu da nuna mubaya’ar aiki tare dashi domin nasara a babban zaben 2023.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *