Korea ta Arewa ta harba makami masu linzami cikin teku na gabashin kasar a Lahadin nan, kwana guda bayan da sojin korea ta Kudu da na Amurka suka  kammala wata gagarumar rawar daji da Amurka a karon farko cikin shekaru 4.

Korea ta Arewa ta kara azama wajen shirin inganta makamanta a cikin wannan shekarar, duk kuwa da cewa tana fama da takunkuman karayar tattalin arziki.


Babban hafsan hafsoshin sojin Korea ta Kudu ya ce sun gano makamai masu linzami 8, masu cin gajeren zango da Korea ta Arewa ta harba a tekun gabashi na kusa da Japan.


Japan ta tabbatar da lamarin, inda ta ce Korea ta Arewa ta yi gwajin  makamai masu linzamin ne a  yankuna da dama, tana mai cewa kasar ta yi gwaje gwaje da dama na makamai a wannan shekarar fiye da yadda ta taba yi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *