Gwamnan Jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya zama dan takarar kujerar Sanata na jam’iyyar PDP mai wakiltar Sokototo ta Kudu.

Mazabar majalisar dattawa ta Sokototo ta Kudu ta kunshi kananan hukumomi bakwai da suka hadarda Bodinga, da Dange/Shuni,da Kebbe, da Shagari, da Tambuwal, da Tureta, da kuma Yabo.


A makon da ya gabata ne gwamnan ya janyewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da aka gudanar a Abuja.


A baya Gwamna Tambuwal ya wakilci mazabar Tambuwal/Kebbe a majalisar wakilai, inda ya zama shugaban majalisar a zangonsa na uku.


Gwamnan na Neman kujerar Sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu,wanda Mohammed Danbaba, wanda kwanan nan ya fice daga PDP zuwa APC.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *