Jajare ya kuma yi zargin cewa gwamnan na siye manyan yan PDP a jihar don kawar da adawa a jihar.
Da yake zantawa da manema labarai a ranar Lahadi, Jajare ya bayyana cewa tsawon shekaru gwamnati mai ci a Borno ta fitar manyan masu fada aji daga PDP don ci gaba da tsarin jam’iyya daya a jihar.
Ya ce da wannan zaben fidda dan takarar shugaban kasa na PDP da aka yi cikin gaskiya da amana wanda ya samar da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a matsayin gwaninta jam’iyyar za ta tabbatar da sukar manufofin gwamnatin APC idan ba zai amfani mutanen Borno kamar yadda yake a kundin tsarin mulki.
Ya ce idan aka zabe shi a matsayin gwamna a 2023, zai dawo da dukkanin ma’aikatan gwamnati da aka sallama sannan ya biya su hakkinsu da aka tauye tsawon shekaru.
A cewarsa, yanayin rashin tsaro a jihar ya kawo wahalhalu da bai kamata ace an yanke ma’aikata daga inda suke samun kudin shiga ba bayan an hana su zuwa gonaki.