Ku saki ‘yayanmu 8 dake hannunku a Yola sai mu saki fasinjojin jirgin kasan Kaduna/Abuja

Yan ta’addan da suka sace fasinjojin jirgin kasan Abuja-Kaduna sun yi barazanar fara kashe wadanda suka kwashe idan gwamnatin tarayya bata saki yaransy dake hannunta ba.

Yan ta’addan da suka sace fasinjojin jirgin kasan Abuja-Kaduna sun yi barazanar fara kashe wadanda suka kwashe idan gwamnatin tarayya bata saki yaransy dake hannunta ba.

Shugaban yan ta’addan, Abu Barrah, yace

Gwamnati ta ajiye ‘yayansu a gidan marayu dake Yola. Abu Barrah ya bayyana hakan ne ga Tukur Mamu, shugaban kamfanin jaridan Desert Herald. Yace: ” ‘Yayanmu guda 8 masu shekaru 1 – 7 na tsare a gidan marayu dake Jimeta, jihar Adamawa karkashin jagorancin hukumar Sojin Najeriya.”

“Sunan ‘yayanmu; Abdulrahman, Bilkisu, Usman, Ibrahim and Juwairiyyah. An kwashesu ne daga hannun matanmu a jihar Nasarawa kuma aka kaisu gidan marayu a Yola.” “Kafin mu saki fasinjojin da cigaba da aikin jirgin kasan, wajibi ne a saki ‘yayanmu.”

Ya kara da cewa idan aka saki ‘yayan na su, zasu saki fasinjoji mata kadai. Yace idan gwamnati bata sake su ba, zasu kashe fasinjojin daya bayan daya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *