Ya nuna alhininsa ne yayin tattaunawa da manema labarai a ranar Juma’a a bangaren jirgin shugaban kasa da ke filin jirgin Nnamdi Azikwe a Abuja, bayan dawowarsa daga Uyo, Jihar Akwa Ibom.
Ya kuma bayyana jin dadinsa akan yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari da Sultan din Sokoto su ka nuna rashin jindadinsu akan lamarin.
Kamar yadda The Punch ta ruwaito, ya kada baki inda ya ce:
Osinbajo ya kwatanta rashin dacewar yadda matasan su ka dauki doka a hannunsu kasancewar akwai hukumar da ya dace a kai wa kara. Ya mika ta’aziyyarsa ga ‘yan uwan mamaciyar tare da fatan Ubangiji ya ba su hakuri.
Ya ci gaba da cewa:
“Ina tunanin irin tashin hankalin da ‘yan uwanta su ka shiga bayan samun labarin mutuwarta da kuma aika-aikar da aka yi mata. “Hakika abin akwai taba zuciya. Mu na yi musu ta’aziyyar tare da fatan Ubangiji ya sanya musu salama a zuciyoyinsu.”