Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya karbi Fom din takara kujerar Sanata na jam’iyyar All Progressives Congress (APC). Dan siyasan mai shekaru 72 a duniya na shirin wakiltar mazabar Kano ta Arewa majalisar dattawan tarayya.
Ganduje, zai kara da Sanata Barau Jibrin wanda ke rike da kujeran tsawon shekaru bakwai yanzu Ganduje ya rike matsayin mataimakin gwamna karkashin Rabiu Kwankwaso 1999-2003 sannan suka sake tafiya tare 2011-2015.