Mahafiyar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata ta rasu.

Rasuwar Malam Fatima, mahaifiyar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata, wanda aka sace sama da shekaru biyu da suka wuce a gidansa da ke unguwar Barnawa a cikin birnin Kaduna.

Rahma Tv ta rahoto cewa ta rasu ne a ranar Talata a Asibitin Sojojin Najeriya na 44 da ke Kaduna inda aka kai ta sakamakon rashin lafiya da ba a bayyana ba.

Wani makusancin iyalan na kut-da-kut, Malam Lawal, wanda amini ne ga wan Dadiyata, Usman Idris, ya tabbatar da cewa a halin yanzu, ’ya’yan marigayiyar na kan hanyarsu ta komawa Kaduna, bayan samun labarin rasuwarta.

Dadiyata, malami a Jami’ar Tarayya Dutsen-Ma, ya bace tun lokacin da aka sace shi, kuma ‘yan uwansa suna rayuwa tare da rashin tabbas game da makomarsa.

Allah SWT Ya jikan ta da Rahma.

One Reply to “Mahafiyar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata ta rasu.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *