Gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin raba hatsi.

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin raba hatsi domin a rage radadin tsadar kayan abinci a kasar nan.

Ministan harkarkoin noma da raya karkara, Mohammad Abubakar ne ya kaddamar da wannan shiri a sansanin yan gudun hijira a Karamiji dake garin birnin tarayya Abuja Mohammad Abubakar yace an zabi wannan wuri ne domin wadanda suke gudun hijira suna cikin wadanda suka fi kowa bukatar kayan abinci a wannan lokaci.

Baya ga hatsi, Ministan ya bayyana cewar sauran kayan da ake rabawa sun hadarda ganye da abincin gidan gona da zasu kawo farashi yayi sauki a kasuwa.

Ministan ya kara da cewar ma’aikatar jin kai da bada agajin gaggawa zata raba tan dubu 12, na wadannan kayan abinci ga mabukata.

One Reply to “Gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin raba hatsi.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *