Masu ruwa da tsaki kan tamaula sun damu da matakan Faransa na dakile Korona

Masu ruwa da tsaki kan tamaula sun bayyana damuwa dangane da rage yawan ‘yan kallon da gwamnatin Faransa ta yi a filayen wasanni da zummar dakile yaduwar annobar Korona, matakin da suka ce zai rage armashin wasannin da ya dawo tun bayan rashin walwalar da suka fuskanta a shekarar 2020, lokacin da annobar ta kai kololuwa.

A baya bayan nan ne dai Firaministan Faransa Jean Castex ya ce daga yanzu ‘yan kallo dubu 5 ne kawai ke da damar shiga filayen wasanni ciki har da na kwallon kafa domin baiwa idanunsu abinci kai tsaye, yayin da kuma adadin mutane dubu 2 za su rika shiga kallon wasannin da ake yi a rufaffun filaye.

Wannan doka dai za ta shafe makwanni uku tana aiki, daga ranar 3 ga watan Janairu.

A ranar Juma’a 7 ga watan na Janairu kuma za a cigaba da wasannin gasar Ligue 1, bayan da sabbin matakan takaita walwala da taron jama’a suka fara aiki, wadanda za su shafi wasannin da za a kara tsakanin Lyon da Paris Saint-Germain a ranar 9 ga wata, wasa mafi girma a a karshen mako, sai kuma karawa tsakanin Lille da Marseille.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *