Yau Olaf Scholz zai karbi ragamar jagorancin kasar Jamus

Yau ake saran Olaf Scholz ya karbi ragamar jagorancin kasar Jamus, abinda zai kawo karshen mulkin shekaru 16 da Angela Merkel keyi da kuma bude wani sabon babi a tarihin kasar.

Wannan zai gudana ne bayan da Majalisar Bendestag ta tabbatar masa da mukamin, daga bisani kuma shugaban kasa Frank-Walter Steinmeier ya rantsar da shi.

Scholz ya rike mukamin ministan kudi a karkashin gwamnatin Merkel kafin samun nasarar zaben da yayi a ranar 26 ga watan Satumbar da ta gabata.

Scholz da wanda zai zama ministan kudi Christian Lindner da ministan tattalin arziki da ministan muhalli Robert Habeck REUTERS – FABRIZIO BENSCH

Sabon shugaban gwamnatin mai shekaru 63 yayi nasarar kulla yarjejeniyar kawancen kafa gwamnati na shekaru 4 da wasu jam’iyyun siyasar kasar, yayin da ya bayyana farin cikin sa da fahimtar junar da suka samu.

Scholz ya zama mataimakin shugaban jam’iyyar sa ta ’Social Democrat‘ a shekarar 1980, amma sai ya gaza jagoracin ta a matsayin shugaba saboda zargin da ake masa na kin goyan bayan manufofin ta sau da kafa.

One Reply to “Yau Olaf Scholz zai karbi ragamar jagorancin kasar Jamus”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *