Faransa ta kame wanda ake zargi da kisan dan jarida Jamal Kashoggi

Jami’an ‘yansandan Faransa sun sanar da kame wani mutum da ke cikin tawagar Saudiyya da ake da zargi da yiwa dan jarida Jamal Kashoggi kisan gilla a Turkiya cikin shekarar 2018.

A yammacin yau talata ne jami’an ‘yan sandan kan iyaka na Faransa suka kame Khalid Alotaibi mai shekaru 33 biyo bayan umarnin kamensa da Turkiyya ta bayar.

Majiyoyin shari’a a Faransa sun ce an kame Alotaibi ne lokacin da ya ke kokarin hawa jirgi zuwa birnin Riyadh na Saudiyya a babban filin jirgin saman a Charles de Gaulle da ke Paris, yayinda zai gurfana gaban shari’a kowanne lokaci a gobe laraba.

A shekarar 2020 ne Turkiya ta fara wasu mutum 20 da ake zargin hannunsu a kisan na Kashoggi ba tare da halartarsu gaban kotu ba, ciki har da tsaffin hadiman Mohammed bin Salman yarima mai jiran gadon sarautar saudiyya 2.

Haka zalika a cikin shekarar nan Turkiya ta kara wasu mutum 6 cikin wadanda ake zargi da kisan dan jaridar na Saudiya Jamal Kashoggi suma dai ba tare da sun je kasar ta Turkiya ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *