Madrid da gwamnatin Ribas sun kulla yarjejeniyar ci gaban wasanni

Real Madrid da Gwamnatin Jihar Ribas dake Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin kai don inganta wasanni tsakanin yara da matasa a Kwalejin Real Madrid a Fatakwal.

A cewar wata sanarwa mai dauke da sa hannun Kelvin Ebiri, Mataimaki na Musamman kan harkokin Yada Labarai ga Gwamnan Jihar Ribas, sanya hannun ya gudana ne a karshen mako a dakin taro na Real Madrid Sport City, dake Madrid na Spain.

REAL MADRID da Gwamnatin Jihar Ribas dake Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tabbatar da hadin kai don inganta wasanni tsakanin yara da matasa a Kwalejin Real Madrid a Fatakwal. 17/10/21.

Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, a madadin Gwamnatin Jihar Ribas da Mista Enrique Sanchez, Mataimakin Shugaban zartarwa, Gidauniyar Real Madrid da Mista Jihad Saade, Shugaba, Interact Sports, ne suka rattaba hannu kan yarjejeniyar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *