Al’ummar Kaduna sun kalubalanci matakan gwamnati na yaki da ‘yan bindiga

Al’umma da dama a jihar Kaduna da ke Najeriya na kokawa dangane da matakan da gwamnatin jihar ta dauka na dakile aikin ‘Yan ta’adda a  jihar inda su ke ganin cewa matakan sunyi tsauri da yawa, kuma suke bukatar a sassauta.

A makon da ya gabata ne dai gwamnatin jihar ta hana hawa babura a fadin jihar har na tsawon watanni uku tare kuma katse layukan sadarwa a wasu sassan jihar.

In kai mazaunin Kaduna ne zamu so muji raayinku, ta hanyar rubutu a kasa.

3 Replies to “Al’ummar Kaduna sun kalubalanci matakan gwamnati na yaki da ‘yan bindiga”

  1. Yakamata abar maso kananan babura suci gaba da hawa baburan su zuwa wajan aikace aikacen su da kuma kai yaransu makaranta domin ko saboda yara da ake dauka zuwa makarantu ya kamata a duba wan nan magana, mun gode allah allah ya baku ikon yin haka amin allah ya kare ka malam nasiru ahmad El rufa’i a duk inda kake.

  2. Gaskiya yakamata, gomnati taduba halinda al umma suke shiga, a sassauta wannan doka,
    Inda abun yafi tsauri, babu irin wannan dokar da akasa a kaduna.
    Zakaga mutane tsofaffi da yara,
    Suna tafiyar almost 2 to 3 kilo meter akasa kuma cikin dare, kowa yana neman dauki wazai tai maka mashi yarage mashi hanya,
    A irin wannan halin aisu yan Ta’addan zasu iya zuwa da mota su faka, dasunan zasu tai maka ma mutane, kuma babu wanda zaice bazai shigaba tunda a wannan lokacin kowa neman taimako yake wlh, babba da yaro, da tsofaffi.
    Kuma barayi suna kwace mashina dasunan jami’an tsaro.
    Dan haka muna kira zuwa ga gomnatin jihar kaduna da tadubi Allah, tallahi halinda mutane sukashiga a wannan jiha tamu mai albarka.
    Muna fata za’a karbi rokonmu.
    Mungode.
    Long life Kaduna state
    And long life the people of kaduna state

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *