‘Yan bindiga sun saki Kwamishinan jihar Neja da suka sace

Masu garkuwa da mutane sun sako Kwamishinan watsa labaran Jihar Neja da ke Najeriya kwanaki biyar bayan sace shi da suka yi.


Sakin Kwamishinan na zuwa ne a yayin da daliban makarantar Islamiyyar Salihu Tanko da ke Tegina suka kwashe fiye da kwanaki 75 a hannun ‘yan bindigar kuma ba tare da sakinsu ba duk kuwa da biyan kudi sama da naira miliyan 50 da iyayen yaran suka yi domin a sako ‘ya’yan nasu.
-RFI

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *