Yan 16 da za su buga zagaye na biyu a Champions League

An samu kungiyoyi 16 da za su buga zagaye na biyu a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Champions League ta bana.

Wadanda suka ja ragamar rukuninsu sun hada da Bayern Munich da Chelsea da Borussia Dortmund da Juventus da Liverpool da Manchester City.

Sauran sun hada da Paris St Germain da kuma Real Madrid.

Wadanda suka yi na biyu a rukunai sun hada da Atalanta da Atletico Madrid da Barcelona da Lazio da RB Leipzig da Borussia Monchengladbach da FC Porto da kuma Sevilla.

Kunyiyoyi uku ne a Ingila suka kai zagayen gaba da suka hada da Manchester City da Chelsea da kuma Liverpool, bayan da ka fitar da Manchester United.

Spaniya kuwa kungiyoyi hudu ne ke wakiltarta da suka hada da Real Madrid da Barcelona da Atletico Madrid da kuma Sevilla.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *